エピソード

  • Inda Aka Mike Da Inda Aka Kauce Tun Bayan Dawowa Mulkin Dimokuraɗiyya A Jamhuriya Ta Hudu
    2026/01/23

    Send us a text

    Kamfanin yaɗa labarai na Media Trust ya daɗe yana taka muhimmiyar rawa wajen buɗe tattaunawa masu ma’ana kan manyan al’amuran da suka shafi tafiyar da ƙasa da dimokuraɗiyya a Najeriya. Daga cikin fitattun shirye-shiryensa akwai muhawarar shekara-shekara da kamfanin ke shirya wa, wadda ta zama wani dandali na musamman da ke haɗa masana, ‘yan siyasa, masana doka, da masu ruwa da tsaki domin nazari da tantance halin da ƙasa ke ciki.


    A bana, wannan muhawara ta kai karo na 23, inda aka zaɓi mayar da hankali kan abin da aka yi daidai da kuma abin da aka kasa yi tun bayan dawowar Najeriya mulkin farar hula a jamhuriya ta huɗu.


    Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci, ya duba sama da shekaru ashirin na tafiyar dimokuraɗiyya, wadanne irin nasarori ko akasin haka aka samu? Shin ko Najeriya ta kai ga ci a kokarinta na cimma muradun dubban yan kasa?

    続きを読む 一部表示
    15 分
  • Nasarori Da Kalubalen Da Bankin Musulunci ke Fuskanta A Najeriya
    2026/01/22

    Send us a text

    A Jamhuriya ta Hudu a Najeriya, wadda ta fara a shekarar 1999, an samu sauye-sauye masu yawa a bangaren tattalin arziki da harkokin kuɗi, ciki har da tasowar bankunan Musulunci. Wannan tsari na banki ya samo asali ne daga buƙatar samar da hanyoyin mu’amala da kuɗi da suka dace da koyarwar addinin Musulunci, wato hanyoyin da ba su ƙunshi riba, da zamba, ko rashin tabbas ba.


    A farkon lokaci, ra’ayin kafa bankunan Musulunci ya fuskanci muhawara da adawa daga wasu ɓangarori na al’umma, musamman saboda fahimtar da ake yi cewa tsarin na da alaƙa da addini. Sai dai daga bisani, gwamnati da hukumomin kula da harkokin banki, musamman Babban Bankin Najeriya (CBN), sun samar da dokoki da ka’idoji da suka bai wa bankunan Musulunci damar aiki a matsayin bankunan da basa cin riba.


    A cigaba da kawo muku shirye shirye gabanin muhawarar Daily Trust, shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi duba ne akan tasowar bankunan musulunci da kalubalen da suke fuskanta.

    続きを読む 一部表示
    25 分
  • Tasirin Siyasar Matasa A Najeriya Tun Bayan Dawowar Jamhuriya Ta Hudu
    2026/01/20

    Send us a text

    Shekaru kafin a sanya hannu kan dokar Not Too Young To Run, siyasar matasa a Najeriya na fuskantar ƙalubale masu tarin yawa. Duk da cewa matasa su ne mafi rinjaye a yawan al’umma da kuma masu katin zaɓe, an dade ana kallonsu ne a matsayin masu ɗaukar tutoci, da yaɗa saƙonni ko kuma masu tayar da tarzoma a lokacin zaɓe, ba tare da ba su cikakkiyar dama ta tsayawa takara ko shiga manyan matakan yanke shawara ba.


    Sai dai a shekarar 2018, bayan sa hannu kan dokar bai wa matasa dama a siyasar Najeriya, an samu sabon salo da fata a fagen siyasa. Dokar ta rage shekarun tsayawa takara a muƙaman siyasa daban-daban, tare da buɗe ƙofa ga matasa masu ƙwazo, da ilimi da kishin ƙasa su shiga fafutukar jagoranci kai tsaye. Wannan mataki ya ƙarfafa gwiwar matasa da dama su fara ganin siyasa a matsayin fagen da za su iya kawo sauyi, ba wai kawai a matsayin masu goyon baya ba.-


    A cigaba da kawo muku shirye gabanin muhawarar Daily Trust, shirin Njaeriya a yau na wannan lokaci zai yi duba ne kan ko yadda siyasar matasa ta kasance a jamhuriya ta hudu tun bayan ayyana wannan doka.

    続きを読む 一部表示
    20 分
  • Yadda Siyasar Ubangida Ta Yi Tasiri Ga Siyasar Najeriya A Jamhuriya Ta Hudu
    2026/01/19

    Send us a text

    Tun bayan dawowar mulkin farar hula a shekarar 1999, siyasar Najeriya ta kasance karkashin inuwar wasu ’yan tsiraru da ake kira iyayen gidan siyasa. Wannan tsari ya ginu ne a kan karfin mutum guda ko rukuni, inda su ke rike da makullin jam’iyya, su tsara wa’adi, su zabi ’yan takara, su kuma yanke hukunci ba tare da la’akari da ra’ayin mafi yawan mambobi ko jama’a ba.


    A Jamhuriya ta Hudu, siyasar ubangida ta zama tamkar al’ada da aka amince da ita, inda dimokuraɗiyya ta hakika ke fuskantar barazana daga siyasar biyayya da ladar mukami. A maimakon gasa ta tunani, da tsari da manufofi, an koma fafatawa ta kusanci da ubangida, wanda hakan ya raunana jam’iyyu, ya haifar da rikice-rikicen cikin gida, tare da jefa talakawa cikin rashin tabbas game da sahihancin zabensu.


    A cigaba da kawo muku shirye shirye gabanin Muhawarar Daily Trust ta 2025, shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi duba ne kan Siyasar Uban gida ya yi tasiri da kuma yadda ya juya akalan siyasar Najeriya tun dawowar jamhuriya ta hudu a Najeriya.

    続きを読む 一部表示
    25 分
  • Untitled Episode
    2026/01/17
    24 分
  • Abun Koyin ‘Yan Siyasa Da Matasa Kan Jarumtar Goodluck Jonathan A 2015
    2026/01/16

    Send us a text

    Kiran wayan da tsohon Shugaban kasa Goodluck Ebele Jonathan ya yi wa marigayi Muhammadu Buhari ta bar tarihi mai muhimmanci a Najeriya.

    Waya da ta kwantar da hankalin kasa, ta kuma dakatar da fargabar tashin hankali.
    A ranar da sakamakon zaben shekarar 2015 ya fara bayyana, tsohon Shugaban Kasa, Goodluck Ebele Jonathan, ya zabi zaman lafiya a kan mulki, ya kuma zabi Najeriya a kan kansa.


    Maimakon ya tada jijiyar wuya, ko ya kalubalanci sakamakon da zai iya haddasa rikici, Goodluck Jonathan ya dauki waya, ya kira abokin takararsa, tsohon shugaban kasa Marigayi Muhammadu Buhari, ya taya shi murnar nasara. Wannan mataki ya nuna jarumtaka, da kishin kasa, da girmama dimokuraɗiyya.


    Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi duba ne kan bajintar da tsohon shugaban kasa Goodluck jonathan ya nuna a tarihin Najeriya.

    続きを読む 一部表示
    19 分
  • Bayan Shekaru Sittin, Me Ya Sa Har Yanzu Ake Tunawa Da Su Sardauna?
    2026/01/15

    Send us a text

    A tarihin kowace ƙasa, akwai wasu mutane da ba lokaci ko sauyin zamani ke iya gogewa daga ƙwaƙwalwar al’umma ba. A Najeriya, waɗannan su ne founding fathers — jagororin da suka tsaya tsayin daka wajen jagorantar gwagwarmayar neman ’yancin kai, kafa tubalan dimokuraɗiyya, da shimfiɗa tsarin ƙasa tun kafin a haifi Jamhuriyar Tarayya ta Najeriya. Gudunmawarsu ba ta tsaya kawai ga siyasa ba; sun bayar da rayuwarsu, tunaninsu domin tabbatar da cewa Najeriya ta zama ƙasa mai cikakken iko da mutunci a idon duniya.


    Ko wadanne dalilai ne suka sa har yanzu ba’a manta da irin wadannan mutane a tarihin Najeriya ba?


    Wannan shine batun da shirin Najeirya A Yau na wannan lokaci zai yi duba a kai.

    続きを読む 一部表示
    22 分
  • Zabukan Da Aka Gudanar Lokacin Dawowar Mulkin Farar Hula A Jamhuriya Ta Hudu
    2026/01/13

    Send us a text

    Bayan kusan shekaru goma sha shida na mulkin soja, Najeriya ta dawo kan tafarkin mulkin farar hula a shekarar 1999, abin da ya buɗe sabon babi a tarihin siyasar ƙasar. Zaɓen da aka gudanar a wannan lokaci shi ne zaɓen farko na Jamhuriya ta Huɗu, inda aka gudanar da zaɓukan kananan hukumomi, majalisun dokoki, gwamnoni da kuma shugaban ƙasa a ƙarƙashin kulawar Hukumar Zaɓe ta Ƙasa, wato INEC.


    Duk da cike da ƙalubale kamar ƙarancin kayan aiki, rashin cikakken shiri, zarge-zargen maguɗin zaɓe da kuma ƙarancin wayar da kan jama’a, zaɓen ya kasance muhimmin mataki na dawo da ikon mulki hannun farar hula. Jama’a da dama sun shiga zaɓen ne da fatan ganin ƙarshen mulkin soja da kafa gwamnati mai wakiltar ra’ayin al’umma.


    Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi waiwaye ne kan zabukan farko da aka gudanar a jamhuriya ta hudu bayan dawowar mulkin farar hula a Najeriya.

    続きを読む 一部表示
    22 分