Inda Aka Mike Da Inda Aka Kauce Tun Bayan Dawowa Mulkin Dimokuraɗiyya A Jamhuriya Ta Hudu
カートのアイテムが多すぎます
カートに追加できませんでした。
ウィッシュリストに追加できませんでした。
ほしい物リストの削除に失敗しました。
ポッドキャストのフォローに失敗しました
ポッドキャストのフォロー解除に失敗しました
-
ナレーター:
-
著者:
概要
Send us a text
Kamfanin yaɗa labarai na Media Trust ya daɗe yana taka muhimmiyar rawa wajen buɗe tattaunawa masu ma’ana kan manyan al’amuran da suka shafi tafiyar da ƙasa da dimokuraɗiyya a Najeriya. Daga cikin fitattun shirye-shiryensa akwai muhawarar shekara-shekara da kamfanin ke shirya wa, wadda ta zama wani dandali na musamman da ke haɗa masana, ‘yan siyasa, masana doka, da masu ruwa da tsaki domin nazari da tantance halin da ƙasa ke ciki.
A bana, wannan muhawara ta kai karo na 23, inda aka zaɓi mayar da hankali kan abin da aka yi daidai da kuma abin da aka kasa yi tun bayan dawowar Najeriya mulkin farar hula a jamhuriya ta huɗu.
Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci, ya duba sama da shekaru ashirin na tafiyar dimokuraɗiyya, wadanne irin nasarori ko akasin haka aka samu? Shin ko Najeriya ta kai ga ci a kokarinta na cimma muradun dubban yan kasa?