『Najeriya a Yau』のカバーアート

Najeriya a Yau

Najeriya a Yau

著者: Muslim Muhammad Yusuf Ummu Salmah Ibrahim
無料で聴く

概要

Shiri ne na minti 15 dake duba na tsanaki, da nazari mai gamsarwa, tare da tsokaci mai amfanarwa, a kan batutuwan da ke ɗaukar hankali a lamuran yau da kullum.

© 2026 Najeriya a Yau
政治・政府 政治学
エピソード
  • Inda Aka Mike Da Inda Aka Kauce Tun Bayan Dawowa Mulkin Dimokuraɗiyya A Jamhuriya Ta Hudu
    2026/01/23

    Send us a text

    Kamfanin yaɗa labarai na Media Trust ya daɗe yana taka muhimmiyar rawa wajen buɗe tattaunawa masu ma’ana kan manyan al’amuran da suka shafi tafiyar da ƙasa da dimokuraɗiyya a Najeriya. Daga cikin fitattun shirye-shiryensa akwai muhawarar shekara-shekara da kamfanin ke shirya wa, wadda ta zama wani dandali na musamman da ke haɗa masana, ‘yan siyasa, masana doka, da masu ruwa da tsaki domin nazari da tantance halin da ƙasa ke ciki.


    A bana, wannan muhawara ta kai karo na 23, inda aka zaɓi mayar da hankali kan abin da aka yi daidai da kuma abin da aka kasa yi tun bayan dawowar Najeriya mulkin farar hula a jamhuriya ta huɗu.


    Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci, ya duba sama da shekaru ashirin na tafiyar dimokuraɗiyya, wadanne irin nasarori ko akasin haka aka samu? Shin ko Najeriya ta kai ga ci a kokarinta na cimma muradun dubban yan kasa?

    続きを読む 一部表示
    15 分
  • Nasarori Da Kalubalen Da Bankin Musulunci ke Fuskanta A Najeriya
    2026/01/22

    Send us a text

    A Jamhuriya ta Hudu a Najeriya, wadda ta fara a shekarar 1999, an samu sauye-sauye masu yawa a bangaren tattalin arziki da harkokin kuɗi, ciki har da tasowar bankunan Musulunci. Wannan tsari na banki ya samo asali ne daga buƙatar samar da hanyoyin mu’amala da kuɗi da suka dace da koyarwar addinin Musulunci, wato hanyoyin da ba su ƙunshi riba, da zamba, ko rashin tabbas ba.


    A farkon lokaci, ra’ayin kafa bankunan Musulunci ya fuskanci muhawara da adawa daga wasu ɓangarori na al’umma, musamman saboda fahimtar da ake yi cewa tsarin na da alaƙa da addini. Sai dai daga bisani, gwamnati da hukumomin kula da harkokin banki, musamman Babban Bankin Najeriya (CBN), sun samar da dokoki da ka’idoji da suka bai wa bankunan Musulunci damar aiki a matsayin bankunan da basa cin riba.


    A cigaba da kawo muku shirye shirye gabanin muhawarar Daily Trust, shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi duba ne akan tasowar bankunan musulunci da kalubalen da suke fuskanta.

    続きを読む 一部表示
    25 分
  • Tasirin Siyasar Matasa A Najeriya Tun Bayan Dawowar Jamhuriya Ta Hudu
    2026/01/20

    Send us a text

    Shekaru kafin a sanya hannu kan dokar Not Too Young To Run, siyasar matasa a Najeriya na fuskantar ƙalubale masu tarin yawa. Duk da cewa matasa su ne mafi rinjaye a yawan al’umma da kuma masu katin zaɓe, an dade ana kallonsu ne a matsayin masu ɗaukar tutoci, da yaɗa saƙonni ko kuma masu tayar da tarzoma a lokacin zaɓe, ba tare da ba su cikakkiyar dama ta tsayawa takara ko shiga manyan matakan yanke shawara ba.


    Sai dai a shekarar 2018, bayan sa hannu kan dokar bai wa matasa dama a siyasar Najeriya, an samu sabon salo da fata a fagen siyasa. Dokar ta rage shekarun tsayawa takara a muƙaman siyasa daban-daban, tare da buɗe ƙofa ga matasa masu ƙwazo, da ilimi da kishin ƙasa su shiga fafutukar jagoranci kai tsaye. Wannan mataki ya ƙarfafa gwiwar matasa da dama su fara ganin siyasa a matsayin fagen da za su iya kawo sauyi, ba wai kawai a matsayin masu goyon baya ba.-


    A cigaba da kawo muku shirye gabanin muhawarar Daily Trust, shirin Njaeriya a yau na wannan lokaci zai yi duba ne kan ko yadda siyasar matasa ta kasance a jamhuriya ta hudu tun bayan ayyana wannan doka.

    続きを読む 一部表示
    20 分
まだレビューはありません