『Daga Laraba』のカバーアート

Daga Laraba

Daga Laraba

無料で聴く

このコンテンツについて

Shiri ne da ke tattaunawa mai zurfi a kan batutuwan da suka shafi al'umma kai-tsaye, da nazari a kan tasirin da za su iya yi, da nemo hanyar magance ko kauce wa illolin da za su iya hifarwa bayan jin ta-bakin wadanda abin ya shafa.

© 2025 Daga Laraba
政治・政府 政治学 社会科学
エピソード
  • Shin Ko Zafin Nema Na Kawo Samu?
    2025/07/09

    Mai yiwuwa masu sauraro sun san wani bawan Allah wanda kusan a kullum, kuksan a ko yaushe a cikin nema yake, amma Allah bai kawo ba..


    Wasu dai na ganin yawan fadi-tashin da mutum yakan yi ba shi ne zai ba shi kudaden da yake bukata ba, yayin da wasu suke ganin jajircewar mutum tana da nasaba da yawan abin da zai samu.


    Shirin Daga Laraba na wannan makon zai yi nazari ne kan kujiba-kujibar da mutane suke yi don samun arziki da tambayar ko zafin nema yana kawo samu?

    続きを読む 一部表示
    19 分
  • Cutukan Da Sinadaran Yin Burodi Ke Haifarwa
    2025/07/02

    Burodi ya zama daya daga cikin abincin da ‘yan Najeriya basa iya yi babu shi. Yayin da wasu ke cin shi a matsayin abin Karin kumallo da safe, wasu kuwa na cin shi a matsayin abincin rana a wasu lokutan ma har da na dare.


    A duk lokacin da aka ce masu sarrafa burodi sun shiga yajin aiki, ko fulawa tayi karanci hakan kan haifar da raguwar burodi a kasuwa wadda kan jefa masu cin shi a cikin mawuyacin hali.


    Shirin Najeriya A Yau na wannan makon zai yi nazari ne kan sinadaran da ake amfani da su wajen sarrafa burodi da kuma irin cutar da suke jawowa.

    続きを読む 一部表示
    29 分
  • Shin Ko Kare Kai Daga Harin ‘Yan Ta’adda Zai Kawo Karshen Matsalar Tsaro?
    2025/06/18

    Hare haren ‘yan ta’adda na kara ta’azzara a yankuna daban daban na fadin kasar nan wanda hakan ke nuni da Karin rashin tsaro da ya dade yana ciwa alumma da ma gwamnati tuwo a kwarya.


    Ko a kwana kwanan nan an ga yadda jihar filato tayi ta fama da irin wadannan hare hare da kuma hare haren ramuwar gayya.

    Wani kididdiga kungiyar dake tattara bayanan hare haren ta’addanci ta fitar ya nuna cewa Najeriya ta taso daga mataki na 8 zuwa na 6 a batun ta’addanci a duniya.

    Kazalika a kwanakin nan wani hari da aka kai a wasu yankunan jihar Binuwe yayi sanadiyyar halakar mutane da dama, wadda hakan ya jawo cece ku ce da ya kai har wasu na kiran mutane su tashi don kare kan su.

    Irin wannan kira dai an dade ana yi, sai dai gwamnati na ganin ba daidai ne mutane su kare kan su daga hare haren ‘yan ta’adda ba.


    Shirin Daga Laraba na wannan mako zai yi nazari ne kan shin ko kare kai daga hare haren ‘yan ta’adda zai kawo karshen matsalar tsaro da ake fuskanta a Najeriya?

    続きを読む 一部表示
    29 分

Daga Larabaに寄せられたリスナーの声

カスタマーレビュー:以下のタブを選択することで、他のサイトのレビューをご覧になれます。